Dangin Uba (21 to 23)


Dangin Uba


DANGIN UBA

Tafiya take kanta a kasa, hannun ta rike yake da Yar karamar jaka Wanda bazai wuce handout biyu bane aciki, a hankali take tafiya hankalin ta kwance har ta Isa inda suke sallama tayi had'e da jaan kujerar dake gefen Haisam ta zauna.






Murmushi Haisam yayi yace "Barka da zuwa the only princess in Haisam Palace"

"Uhmn Yaya Kenan princess kawai ashe da saura na"

"Wa ya gaya miki? Ke Kanki kin San ke ta dabance"

Murmushi tayi sai Yanzu ta maida kallon ta ga su Aysha dake aikin kallon ta Murmushi tayi Tace "Sannun ku fa"

Mardiya ce ta amsa da "yauwa"

Ganin Aysha tayi nisa a tunani ta d'an tab'a ta, a d'an razane Tace "Yauwa sannu ya kike"

"Lafiya Lau"

Haisam yace "Princess meet Aysha and Aysha this is My princess bani da tamkar ta a Rayuwa"

Kirkirerren Murmushi Aysha tayi Tace "Nice To meet you, to Amma ita d'in bata da suna ne?

Haisam Yar karamar dariya yayi yace "Tana dashi Mana kawai dai sunan ne yayi min nauyi bana iya Kiran sa sai on special occasions"

Aysha zaro Ido tayi sannan Kuma ta tab'e baki had'e da girgiza Kai Tace "oh lallai"

Yace "Sai dai idan ita zata fad'a miki da bakin ta"

Aysha Tace "Ya sunan ki?"

"Ma'isha"kawai Tace a takaice.

"Suna Mai dad'i"

" Thank you"

Ma'isha ta maida kallon ta ga Farukh da aikin cin abincin sa kawai yake, Ma'isha dariya tayi Tace "Haba Ya Farukh duk don Kar naci ne kake ta sauri ko?"

Sai da yasa hannu ya kurb'i ruwa kana yace "Na Isa Ma'isha kawai dai naga baku da niyar gama surutun nakune kin San ance kowa da damuwar sa Ni abincin ne damuwa ta"

Haisam yace "Zaka ji da shi ai"

Cikin sanyin Murya Tace "Yaya My promise yunwa nake ji"

"Me Zaki ci?"

"Ka zab'a min komai ma nikam"

"To kin San Ni abinci na d'ayane idan Zaki ci sai a kawo miki"

"Ai Yaya tun bana son chips ka sa na Fara son shi"

Murmushi yayi yace "Barka na kinnga ko ba komai Zaki Rika yi Mana a gida"

Murmushi kawai tayi Nan da Nan yasa aka kawo Mata ta hau ci, har ya karb'i spoon d'in ya Fara Bata baki.







Aisha kamar zata had'iyi ranta ta Rasa abinda yake Mata dad'i tsinta kanta tayi da mikewa ta bar wurin ba tare da Tace komai ba, mardiya ma ta bi bayan ta.

Haisam kuwa bai ma San sun tafi ba , Yana Nan Yana feeding princess d'insa Saida taci ta koshi ya lura ba su Nan, kallon Farukh yayi dake Kallo a wayar sa yace "Haa'ah yaushe Kuma suka tafi?"

"To ka Zama Romeo ina zaka ji tafiyar su? Duk da ma na ga Kamar sauri suke don Nima ba kulani sukayi ba suka tafi"

Tab'e baki yayi ya d'aga kafad'ar sa irin halin ko in kula d'in Nan ya maida kallon sa ga Ma'isha yace "Karfe nawa zaki gama lectures d'in?"

"Karfe 4"

"Ni Kuma sai 6 ya zamuyi Kenan? Zaki jirani ko Zaki koma da napep don bazan barki Kiri driving ba"

d'an turo baki tayi Tace "sabida me Yaya?"

"Umarnin daddy ne, akan Kar na barki kiyi driving sai kin Kara girma"

"Yanzun wai ni yarinya ce?"

"Yes Mana sosai ma Amma..... "

Farukh ne ya dakatar dashi da fad'in "Malam kana da niyar Shiga lectures d'in Nan kuwa ko kuma na tafi na Barka da kanwar ka ku gama surutu?"

"A a tashi muje, princess ki jirani kinji?"

Kai ta d'aga Masa alamun to basu fita ba sai da ya biya su kud'in su, a tare suka fita ta nufi Lt din da zata yi lectures Suma suka nufi nasu.









'Bangaren Su Aisha

Aysha Rai a 'bace ta nufi garden d'in cikin makaranta inda d'alibai sukan zauna su Sha iska, wasu suna karatu wasu Kuma hirar su suke Maza da mata.

Zama tayi ta dafe kanta da hannun bibbiyu, ji take kanta ba tsarawa Kamar zai rabj gida biyu, mardiya ce ta zauna a gefen ta tana kallon ta ba tare da tace Mata kala ba.

Aysha ta d'ago kanta ta kalli mardiya kana ta maida kanta kasa cikin Muryar kuka Tace "Mardiya I need your help ki taimaka min wallahi Ina son gayen Nan har cikin Raina Dan Allah give me advice"

Cike da mamaki take kallon ta tunda ta Fara maganar,Baki a bud'e ta ce" Wai ke dama dagaske son gayen Nan kike?"

Hararar ta tayi Tace "Eh Mana"

"ikon Allah Amma ya akayi Haka bayan ranar Asabar d'in Nan kika ce min kun had'u ko dama kin San shine?"

"Ba wani sanin sa nayi ba, kawai dai ina yawan ganin sa a cafe ne tun ina ji yana burgeni har naji na fara son sa, ranar Asabar d'in ne Naji bazan iya jurewa ba na tinkare sa har na samu damar karb'an Number sa"

Kad'a Kai mardiya tayi had'e da fad'in "Eh lallai gayen Nan na daban ne, nifa duk tunani na shi ya tinkare ki ashe kece, Amma wallahi ba girman ki bane ki zauna kina kuka akan na miji ba, ki dube ki fa kyakkyawa dake babu na mijin da bazai so ki ba sabida kina da duk qualities na kyau"

"Hmm mardiya Kenan ai wallahi duk kyawuna yau da naga yarinyar Nan na Raina Kai na, kamar ita tayi kanta,moreover ki ga yanda yake rawar jikin akanta, alamu sun nuna Yana sonta sosai.







"Gaskiya Allah yayi halitta a wurin Nan,kamar ka sace ta,Amma Ni a gani na ai wannan ba babbar matsala bace ba, kawai ki mata snatching just shot your short, Amma kamin Nan ki fara tabbatar da cewar ba Soyayya suke ba tukunna"

Cikin damuwa ta maraice fuska Tace "Tayaya Kenan zanyi hakan? Guy d'in Nan fa haryanzu ba wani sake min yayi ba bare har na sa ran samun soyayyar sa"

"hmm Qawata Kennan, sai kace ba mace ba ai kiransa kawai zakiyi cikin dabara irin Tamu ta mata Zaki tambaye sa"

"Shikenan zan kirasa zuwa anjima insha Allah"

"Yauwa ko kefe, idan Kuma bamu samu yanda muke so ba sai mu had'a shi da malamai su mana maganin sa"

Wata shu'umin dariya sukayi suka tafa Aysha Tace "Shegur Qawata shiyasa nake yinki ta hannun damana"

Dariya mardiya tayi Tace "Sa wasa ni d'in ai ba daga Nan ba"

"Tabbas Ni shaidace"

Mardiya Tace "Ya labarin mutuminki?"

"Wa Kenan fa?"

"Wa kuwa banda Abdul"

Doguwar tsaki tayi tace "Please spare me wa ke ta tashi Yanzu?"

"Hahahaha Qawata ba ji,kice Haisam ke ruling yanzu"

"ai fad'a ma 'batawa,shi Yana ruling anan" ta nuna kirjin ta,ta d'aura da fad'in "Shi kuma wachan Abu ke ruling a tasa zuciyar"

"hahaha ki yayyafawa zuciyar ki ruwan sanyi Qawata Haisam da kansa zai nemi soyayyar ki, alkawarina ne wannan"

"Nagode Qawata"

Mikewa Tayi Tace "mu  tafi ko?" 

Cikin rashin fahimta mardiya Tace "Ina zamuje?"

"Gida Man"

"Lectures d'infa"

"na yafe" tana kaina ta fara tafiya,bakiea bud'e mardiya ke kallonta,ganin da Gaske take ta Mike ta bi bayanyanta da d'an sauri had'e da gudu, motar Aysha suka nufa,tada motar tayi suka bar cikin school d'in, dropping d'in mardiya tayi kana ta wuce gida,dage unguwar su d'aya hatta layin su ma d'aya hakan yasa bata 'bata lokaci ba ta isa gida.







Karfe 4:10pm

Bayan ta gama lectures ta tsaya jiran sa har sai karfe 6 da Yan mintuna ya Zo suka Kama hanyar gida, yana driving sunan sharar hirar su.

Chan Tace "Yaya Ayshan Nan a ajinku take ne?"

"a'a Yar aji d'ayane?"

"To how comes Kuka Saba?"

"Sabawa a hakan? It's just this Saturday muka had'u fa, itace ma ta karb'i number na"

"sabida me?"

"Wai so take na Zama Tutor d'inta"

"Tutor kuma, Kuma ya yarda Yaya?"

" So kike nace Mata bazaiyu ba? Nifa Musulmi ne itama haka so hakkina ne Akan taimakawa ko wani Musulmi tunda ina da halin taimaka Mata me zai Hana naki amincewa"

Iska ta hura Tace "Hakane"

"Amma irin tambayoyi Haka princess am I safe?"

Murmushin yake tayi Tace "You're safe Mana Yaya, kawai dai naga sai aikin kallon ka take Kuma bata ji dad'in bani abinci a Baki ba, nayi tunanin ma itace auntyn tawa"

Dariya yayi yace "Haba princess ai da kece Zaki Fara sanin hakan,ni ba Soyayya muke da ita ba,hasali ma ban tab'a zaman minti 30 da ita ba"

"Amma fa Yaya Na lura Kamar son ka take"

"ah haba Dan Allah?"

"Allah kuwa"

"Lalle d'an Ni d'in Nan?"

Murmushi kawai tayi yace "Well bani da wannan lokacin Yanzu idan na tashi soyayyar ma ke zansa ki nema min Matar aure"

" Kamar dagaske"

"Allah kuwa dagaske nake miki na rantse miki da kauyen kakana"

Dariya tayi sosai Harda tafi, a Haka suna Hira har suka Isa gida.







Har cikin ranta taji dad'i ko ba komai hankalin ta ya kwanta, tunda tasan ba sonta yake ba, Bata da sauran damu sai na soyayyar sa da fatan ya fahimci hakan.

Suna isa gida suka tarar da su Mummy da Umma shigowar su gidan Kenan Suma, bayan sun gaisa ta wuce d'akin ta Shima Haisam ya wuce nasa d'akin, dake dukkanin su biyu suna da assignment basuyi kallon da suka Saba ba, hatta chat d'in ma basuyi ba.

Haisam na zaune akan gadon sa yana browsing yaga shigowar  Kira ba  wayarsa kallon time yayi yaga Karfe 11:38pm a bayyane yace "Aysha da Daren Nan?"

Picking yayi ya Kara a kunnen sa daga d'ayan 'bangaren tace "Barka da war haka yallab'ai"

Murmushi yayi yace "Yauwa Barka dai Yallab'iya"

Yar karamar dariya tayi Tace "da fatan dai ba bacci Kake ma tashe ka ba?"

"umm umm ba bacci nake ba, assignment nake yi"

"Oh so sorry na dame ka,duk da ma na ce ka Zama Tutor d'ina kaki ko?"

"No Kar ki damu, ba ki nayi ba ai na fad'a miki idan kin shirya ki Sanar dani"

" To na shirya gobe idan Allah ya Kaiimu"

"To Allah ya Kaiimu"

Ta amsa da "Ameen ya Allah"

Yace   "ya  kike d'azu kawai Kika tafi ba sallama"

"Uhmnn gani nayi ka fad'a lambun soyayya baka ji baka gani"

Dariya yayi yace "Soyayya Kuma Ni d'in?"

"Eh Mana Kai da princess d'inka harfa abinci naga kae Bata, nace lallai kud'in masoyan asaline"

Girgiza Kai yayi Kamar tana gaban sa yace "Ni ba Soyayya nake ba"

"Kiyayayya Kake yi Kennan?"

"Hahaha a a, to Shima dai d'an uwan soyayyar ne, amma taya za'ayi nayi soyayya da Kanwata?"

Cikee da farin ciki tace " Au dama kanwar kace? "

"Eh kanwatace da me Kika d'auka?"

"Na d'auka budurwar ka ce"

"To ki ajiye Kanwata ce,ai Ni bank da budurwa ban ma tab'a soyayya ba"

"Na dai ji ban yarda ba"

"Allah kuwa trust me ba wasa nake Miki ba,sai dai idan ke zaki nema min Yanzu"

"A a idan Kuma na nema maka waccce Bata maka ba Kuma fa?"

"Zata ma yi insha Allahu"

"To Insha Allah zan nema maka waccce zata dace da kai"

"Da kuwa naji dad'i sosai"

Nan sukayi ta hirar su kusan na mintuna 20 kana ta Masa sai da safe suka sauke wayar a tare, kwanciyar ta tayi yayin da Haisam ya cigaba da abinda yake yi.


Post a Comment

Previous Post Next Post